Rikici: Dan Majalisar NNPP ya zargi Sanusi Bature da yi wa Gwamnan Kano zagon kasa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Dan majalisar wakilai Mai wakiltar kananan hukumomin Dawakin Tofa, Tofa da Rimin Gado Engr. Tijjani Abdulkadir Jobe ya zargi mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa da yi wa gwamna da yan jam’iyyar NNPP zagon kasa a yankin da ya fito.

Cikin wani fefen bidiyo da Kadaura24 ta kalli, mun hangi Jobe yana wata ganawa da magoya bayansa, inda yake bayyana Daraktan yada labaran Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, a matsayin mai yiwa Jam’iyya zagon kasa, ta hanyar hada kai da dan gidan tsohon Gwamnan Kano, Umar Abdullahi Umar (Abba Ganduje).

IMG 20250415 WA0003
Talla

Jobe yace lallai ya kamata Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya dauki mataki akan Sanusi Bature, domin baya wakiltarsa kuma baya wakiltar jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Kwankwaso Ya Karbi Magoya Bayan Kawu Sumaila sama da 1,200 da su ka koma NNPP

” Ina kira ga Mai girma gwamnan da ka ja kunne mai magana da yawunka Sanusi Bature Dawakin Tofa saboda yana hada Kai da ya’yan Ganduje da gwaggo wajen kawo Rikici a jam’iyyarmu ta NNPP musamman a yankin mu na kananan hukumomin Dawakin Tofa, Tofa da Rimin Gado”. Inji

A baya bayan nan dai, an ga yadda magoya baya ke dafifi a Gidan Sanusi Bature, domin yi masa fatan alheri akan wakilcin yankin a shekarar 2027 mai zuwa.

InShot 20250309 102403344

Kadaura24 ta tuntubi Mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa domin Jin ta bakinsa Kan zargin da Jobe ya yi masa, Amma bai daga wayar da muka buga masa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abun Alkhairin da mataimakin gwamnan Kano ya yi min ba a taba yin min shi a duniya ba – Kabiru D Bello

Tsohon Dan takarar shugaban karamar hukumar Gwarzo Alhaji Kabiru...

Gidajen Wasanni a Kano sun bi ka’idojin da muka sanya musu yayin bikin sallah – Abba El-Mustapah

Daga Rahama Umar Kwaru   A wani bangare na kokarin tabbatar...

Mijina bai yi sata ba kuma kudin da ya tara wa Nijeriya duk an wawashe su – Maryam Abacha

    Maryam Abacha, matar marigayi Janar Sani Abacha, tsohon shugaban...

Matsalar Ruwan: Shugaban K/H Wudil ya ba da Umarnin gyara rijiyoyin burtsatse 100 a yankin

Daga Rahama Umar Kwaru   Shugaban karamar hukumar wudil Hon. Abba...