Rikici: Dan Majalisar NNPP ya zargi Sanusi Bature da yi wa Gwamnan Kano zagon kasa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Dan majalisar wakilai Mai wakiltar kananan hukumomin Dawakin Tofa, Tofa da Rimin Gado Engr. Tijjani Abdulkadir Jobe ya zargi mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa da yi wa gwamna da yan jam’iyyar NNPP zagon kasa a yankin da ya fito.

Cikin wani fefen bidiyo da Kadaura24 ta kalli, mun hangi Jobe yana wata ganawa da magoya bayansa, inda yake bayyana Daraktan yada labaran Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, a matsayin mai yiwa Jam’iyya zagon kasa, ta hanyar hada kai da dan gidan tsohon Gwamnan Kano, Umar Abdullahi Umar (Abba Ganduje).

IMG 20250415 WA0003
Talla

Jobe yace lallai ya kamata Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya dauki mataki akan Sanusi Bature, domin baya wakiltarsa kuma baya wakiltar jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Kwankwaso Ya Karbi Magoya Bayan Kawu Sumaila sama da 1,200 da su ka koma NNPP

” Ina kira ga Mai girma gwamnan da ka ja kunne mai magana da yawunka Sanusi Bature Dawakin Tofa saboda yana hada Kai da ya’yan Ganduje da gwaggo wajen kawo Rikici a jam’iyyarmu ta NNPP musamman a yankin mu na kananan hukumomin Dawakin Tofa, Tofa da Rimin Gado”. Inji

A baya bayan nan dai, an ga yadda magoya baya ke dafifi a Gidan Sanusi Bature, domin yi masa fatan alheri akan wakilcin yankin a shekarar 2027 mai zuwa.

InShot 20250309 102403344

Kadaura24 ta tuntubi Mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa domin Jin ta bakinsa Kan zargin da Jobe ya yi masa, Amma bai daga wayar da muka buga masa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...