Daga Rukayya Abdullahi Maida
Kwamishinan ma’aikatar yada labarai da harkokin cikin gida, ta jihar Kano Com. Ibrahim Abdullahi Waiya ya bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da Wannan lokaci na bikin sallah wajen yiwa Shugabannin addu’o’in samun nasara gudanar da aiyukan da za su inganta rayuwar al’ummar.
Kwamishina Waiya ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu da kansa kuma ya aikowa jaridar Kadaura24.

“Wannan lokaci ne mai daraja da na ke rokon Allah madaukakin Sarki ya ci gaba da yi wa mai girma jagora ya ba shi ikon sauke nauyin al’ummar jihar Kano suka dora masa”.
Sallah: Ku sanya Kano da Nigeria a addu’o’inku na wannan lokacin – Kano ALGON ga jama’a
Ina kuma taya gwamna Abba Kabiru Yusuf da Mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, murnar Barka da Sallah ya Allah ya sake maimaita mana cikin koshin lafiya da kuzari.
Ya ce yana mika gaisuwarsa ta Sallah ga Jagora Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II; da Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano da Masu Girma ‘Yan Majalisar Tarayya daga Kano; da kuma abokan aikina masu girma yan majalisar zartarwa ta jihar Kano.