Rashin wadataccen Abinchi ne ke haifar matsalolin tsaro da tattalin arzikin a Nigeria – Shugaban ACreasal

Date:

Daga Kamal Umar

 

Babban jami’in Shirin bankin duniya mai kula da zaizayar kasa, madatsun ruwa da albarkatun noma wato Acreasal na jihar Yobe Shehu Alhaji Muhammed, ya ce rashin wadataccen abinci wato food security ga al’ummar najeriya shi ne kashin bayan matsalar tsaro, tabarbarewar tattalin arziki, da matsanancin halin da ‘yan kasar suke ciki.

Jami’in ya bayyana haka ne a wajen taron karrama muhimman mutane a kasar nan da lambobin yabo, wanda kungiyar Wazobia mai rajin tabbatar da Shugabancin na gari da sasanta rikici tsakanin kabilu ta shirya.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Shi ma Shugaban kungiyar gamayyar direbobin Najeriya GDN Sadik Abdullahi Jada wanda aka karrama shi saboda jagoranci abin koyi da kungiyar ta su take yi a fannin tuki ta hanyar wayar da kan direbobi da taimakon juna hadi da rungumar ‘ya’yan abokan aikin su wadanda suka hadu ajalin su ta sanadin tukin, ya ce lambar yabon da aka bashi zata yi masa kaimi wajen ci gaba da zage damtse akan kungiyar ta su ta hanyar fadada ayyukan ta.

InShot 20250309 102403344

Adullahi Ahmed Yola, shi ne mataimaki na 1 ga shugaban kungiyar ta gamayyar direbobin najeriya GDN, yayi kira ga abokan aikin su da su tabbatar suna gabatar da ayyukan su bisa kwarewa da bin dokoki domin tsira da mutunci da kaucewa fadawa matsala, tare da bukatar su da su tabbata suna shiga kungiyoyin tuki domin kara samun kariya.

Kungiyar kafafen yada labaran yanar gizo ta bukaci gwamnatin Kano ta gyara hanyoyin dake karkara

Wakilin Kadaura24 ya rawaito cewar taron karramawar wanda ya gudana a nan Kano, ya shaida yadda kungiyar ta karrama sama da mutane 40 daga sassa daban-daban na kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...