Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

Date:

 

Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu da kuma jam’iyya mai mulki ta APC dangane da wasu kalaman suka da dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi a kwanakin baya.

Jam’iyyar ta gargadi Kwankwaso da kada ya kara amfani da sunanta wajen sukar Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC, tana mai cewa tsohon gwamnan jihar Kano an kore shi daga NNPP tuni.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A wata sanarwa da sakataren yada labarai na kasa na NNPP, Dakta Oginni Olaposi, ya fitar a ranar Lahadi a Legas, jam’iyyar ta nesanta kanta daga kalaman Kwankwaso, inda ta bayyana cewa an katse duk wata alaka tsakaninta da Kwankwaso da kuma kungiyar Kwankwasiyya da yake jagoranta.

Da Ɗumi-Ɗumi: Labarin da ake yadawa kan matsayar siyasa ta ba gaskiya ba ne – Kwankwaso

“Muna neman afuwa ga Shugaban kasa Bola Tinubu da dukan iyalan jam’iyyar APC, karkashin jagorancin Dakta Abdullahi Ganduje, bisa cin mutunci da kalaman batanci da Kwankwaso ya furta,” in ji Olaposi.

InShot 20250309 102403344

“Kwankwaso ya daina bayyana kansa a matsayin dan jam’iyyar NNPP da kuma amfani da sunanta wajen kai hari ga jam’iyyar APC da fadar shugaban kasa,” in ji shi. “An kore shi tun tuni, kuma maimakon ya zargi wasu, ya duba kansa idan mabiyansa suna komawa APC.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...