Yadda manoma a Kano suka zargi jami’an Civil defense da karbar kudade a wajensu

Date:

Daga Umar Ibrahim kyarana

 

Manoman dajin dansoshiya dake karamar hukumar Kiru a jihar Kano, sun koka da yadda jami’an tsaron Civil defense ke cin zarafinsu saboda sun je gonakin domin sharewa don fara shirin tunkarar damuwar bana dake tafe.

Wani Manomi mai suna Abdullahi Umar kwida ya zanta da jaridar Kadaura24, ya ce sun ya je gonarsu dake dajin dansoshiya domin ya shareta, kawai sai yan civil defense suka ce sun kama su, su ka kuma tafi da su wani gida inda achan su ka ce sun ci tararsu Naira dubu 300 amma daga bisani suka biya naira dubu 70-70 .

IMG 20250415 WA0003
Talla

Ya ce sana’ar noma ita kadai suka iya kuma ita suke yi, amma yan civil defense na kokarin ta dole sai sun hana su yin noman da su ke yi a dajin duk da cewa Karamar hukumar kira ita ce ta ba su damar yin noma a dajin don hana batagari zama a cikin dajin.

Shi ma wani manomi mai suna Rabi’u Ibrahim Madaki ya shaidawa jaridar Kadaura24 cewa shi ma an kama shi ya na tsaka da share gonarsa, inda aka kai shi wancan gida kuma aka ce an ci tararsa Naira dubu 55, haka ya biya saboda ba yadda zai yi.

Gwamnatin Jihar Kano ta Kaddamar da Kwamitin Gyare-gyare a ma’aikatar Lafiya

“Muna kira ga gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da ya sanya ba ki kan wannan zaluncin da ake yi mana, saboda mun san shi ba ya goyan bayan zalunci”.Inji shi

Shi kuwa Muhammad Bello Dan daji cewa ya yi Naira dubu 20 yan civil defense din suka karba a wurinsa da sunan tara, saboda sun same shi yana share gonarsa dake dajin dansoshiya a karamar hukumar Kiru.

Manoman sun roki Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da ya kai musu dauki saboda cin zarafinsu da ake yi, da kuma yadda ake karbar kudade a hannun su ba bisa ka’ida ba.

InShot 20250309 102403344

Jaridar Kadaura24 ta tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar civil defense dake jihar Kano SC Ibrahim Abdullahi don jin shin rundunar ce ta ba da ikon a rika karbar wadancan kudade a hannun manoman Koko jami’an ne suke gaban kansu.

Ya shaida mana cewa ba su da masaniya kan wadancan kudin da ake zargin jami’ansu suna karba , amma ya ce za su bincika sannan su sanar da Kadaura24 sakamakon binciken da inda ya kammala.

Ku biyo mu za mu cigaba da bibiyar wannan lamari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya Naɗa Ahmed Musa a Matsayin Janar Manaja na Kano Pillars

Daga Zakaria Adam Jigirya   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...