Kungiyar FULDAN ta bukaci gwamnatin tarayya ta kawo karshen rikice-rikice a yankun da Fulani ke rayuwa

Date:

Ahmad Hamisu Gwale

Kungiyar Fulani ta FULDAN, ta bukaci gwamnatin tarayya ta fido da sabbin hanyoyin magance rikice-rikicen da ake samu a wasu yankun da Fulani da kuma makiyaya suke rayuwa.

A wani taron shugabannin kungiyar na shiyyar arewa maso yamma da aka gudanar a Kano a karshen mako, FULDAN ta ce magance matsalar zai kawo zaman lafiya.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Alhaji Muhammad Bello Dan Umma shugaban kungiyar na kasa, ya ce yanzu haka suna ta kokarin ganin an farfado da dangantakar dake tsakanin masu madafun iko wadanda suka fito daga cikin Fulani.

Ya kuma bukaci shugabannin kungiyar na jihohin arewa maso yamma, da su yi hobbasa wajen hada hannu da gwamnati domin samar da masahala ga makiyaya, tare da magance rikice-rikice a tsakanin su.

“Akwai bukatar a fahimci Fulani mutane ne masu son zaman lafiya, amma kowanne lokaci idan abu ya faru sai dora alhakin a kansu, wanda hakan rashin adalci ne”.

Gwamnatin mu ba wajen zaman Barayi ba ce – Gwamnan Kano Abba

Cikin wadanda suka gabatar da jawabai a taron akwai tsohon shugaban kungiyar na riko Alhaji Muhammad Dan Ali, wanda yace ilimantar da Fulani zai taka rawa wajen magance fadawar su cikin rikici.

Dan Ali ya kuma ce mafi yawancin wasu cikin shafaffu da mai ne a kasar nan, nada hannu a wasu rikice-rikicen da suke faruwa a sannan kasar nan.

InShot 20250309 102403344

Shima shugaban kungiyar FULDAN a Kano, Sani Adamu Dakata ya mika sakon godiyarsa ga wadanda suka halarci taron.

Taron shugabannin kungiyar FULDAN na shiyyar arewa maso yammacin Najeriya, ya samu halartar shugabannin yankin wadanda suka fito daga jihohin Kano, Jigawa, Katsina da Kebbi, sai Kaduna da zamfara da kuma Sokoto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin ya sa Bakwana ya fi kowa dacewar ya zama shugaban APC na Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Yawan jama'a da kuma shiga lamuran...

Ba mafita ga yi wa Bello Turji Afuwa – kungiyar Hausawan Nigeria

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Kungiyar Hausawan Nigeria ta ce ba...

Hakimin Kawaji ya yabawa al’ummar Gwagwarwa saboda biyayyarsu ga Shugabanni

Daga Isa Abdullahi Aliyu   Hakimin Kawaji, 𝗔𝗹𝗵𝗮𝗷𝗶 Ibrahim Ado Bayero...

Kungiyar ATM Gwarzo ta bayyana matsayarta akan Tinubu da Gawuna/Garo da Babangandu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kungiyar ATM Gwarzo Organisation, wata kungiya...