Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Date:

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji a jihar Kano, ya sanar da komawarsa jam’iyyar APC a hukumance tare da abokinsa ɗan majalisar wakilai Rt. Hon. Sagir Koki, mai wakiltar Birnin Kano da kewaye.

A cewar Jibrin Kofa, an karɓe su hannu biyu-biyu a zauren majalisar wakilai daga manyan jami’an gwamnati da jam’iyyar APC. A wajen tarbar akwai Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin; Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila; Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda; tsohon Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje; da kuma wasu fitattun jagororin jam’iyyar daga Kano da fadin ƙasar.

InShot 20250309 102512486

Jibrin ya bayyana godiya ta musamman ga Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, da sauran ‘yan majalisa da sanatoci bisa kyakkyawar tarbar da suka yi musu. Ya ce za su ci gaba da aiki tare da sauran ‘yan jam’iyyar domin ci gaban ƙasa cikin jajircewa da sadaukarwa.

Idan za a iya tunawa Dan majalisar tun a ranar laraba ya tara magoya bayansa na kananan hukumomin kiru da Bebeji domin neman shawararsu kuma suka Amince a koma APC , wanda Kofa ya tabbatar da hakan a zauren majalisar wakilai ta Kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...