Gwamnatin mu ba wajen zaman Barayi ba ce – Gwamnan Kano Abba

Date:

 

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatin sa ba wajen zaman ɓarayi ba ce sabo da jajircewa wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.

Da ya ke jawabi a wajen taro da kansilolin mazaɓu 484 da ke gudana yanzu haka a gidan gwamnati, Gwamna Yusuf ya ce gwamnatin sa ba za ta lamunci satar kudin al’umma ba.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A cewar sa, ya na jagorantar gwamnati mai tsafta da kaffa-kaffa wajen sace kudin al’umma, inda ya jaddada cewa “ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu”.

Kungiyar Kwadago ta Kano ta aikewa gwamna Abba gida-gida muhimmin sako

 

Ya ce wannan kokarin yaki da din hanci ne ya sanya gwamnatin ke samun makudan kuɗaɗen da ta ke ta bijiro da aiyuka domin jin dadin al’ummar Kano.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa Gwamna Yusuf ya fadi hakan ne bayan da a kwanan nan tsohon sakataren gwamnatin, Dakta Abdullahi Baffa Bichi ya ke zargin badakala da wawure kuɗaɗen al’umma da gwamnatin ke yi.

InShot 20250309 102403344

A zarge-zargen sa da kafofin watsa labarai su ka yada, Bichi ya yi zargin cewa an cire shi daga sakataren gwamnatin ne saboda ya ki amincewa da a rika” kwashe Naira biliyan 2 ana sakawa a asusun tsohon gwamnan jihar kuma jagoran darikar Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...