Gwamnatin mu ba wajen zaman Barayi ba ce – Gwamnan Kano Abba

Date:

 

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatin sa ba wajen zaman ɓarayi ba ce sabo da jajircewa wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.

Da ya ke jawabi a wajen taro da kansilolin mazaɓu 484 da ke gudana yanzu haka a gidan gwamnati, Gwamna Yusuf ya ce gwamnatin sa ba za ta lamunci satar kudin al’umma ba.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A cewar sa, ya na jagorantar gwamnati mai tsafta da kaffa-kaffa wajen sace kudin al’umma, inda ya jaddada cewa “ɓarawo ba ya zama a gwamnatin mu”.

Kungiyar Kwadago ta Kano ta aikewa gwamna Abba gida-gida muhimmin sako

 

Ya ce wannan kokarin yaki da din hanci ne ya sanya gwamnatin ke samun makudan kuɗaɗen da ta ke ta bijiro da aiyuka domin jin dadin al’ummar Kano.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa Gwamna Yusuf ya fadi hakan ne bayan da a kwanan nan tsohon sakataren gwamnatin, Dakta Abdullahi Baffa Bichi ya ke zargin badakala da wawure kuɗaɗen al’umma da gwamnatin ke yi.

InShot 20250309 102403344

A zarge-zargen sa da kafofin watsa labarai su ka yada, Bichi ya yi zargin cewa an cire shi daga sakataren gwamnatin ne saboda ya ki amincewa da a rika” kwashe Naira biliyan 2 ana sakawa a asusun tsohon gwamnan jihar kuma jagoran darikar Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...