A shirye na ke na yi bayani dalla-dalla, saboda na yi aiki na tsakani da Allah – Mele Kyari

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Tsohon Shugaban Rukunin Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), Mele Kolo Kyari ya bayyana cewa ya yi aikinsa da tsoron Allah.

Tun bayan babban sauyin da aka yi a kamfanin mai, rahotanni daban-daban sun fara yawo game da lokacin mulkin tsohon shugaban.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Daily Trust ta rawaito cewa wani rahoto ya nuna cewa an gano Naira biliyan 80 a asusun wani daga cikin daraktocin matatar mai da aka sauke, wanda ya yi aiki ƙarƙashin Kyari.

Zargin badakala: Ka fito ka fasa kwan, in ka ki mu fasa maka mugunya- Waiya ga Baffa Bichi

Bayo Ojulari, wanda ya gaji Kyari a matsayin shugaban rukunin kamfanin, ya fara babban sauyi wanda ya haifar da ficewar mutane da dama da suka yi aiki ƙarƙashin Kyari.

Haka kuma, an rawaito zarge-zargen cin hanci da rashawa daban-daban da su ka faru a lokacin da ya ke kan mulki.

InShot 20250309 102403344

Sai dai a yayin da ya ke mayar da martani kan wani rahoto da ya ce ya na hannun Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), Kyari ya ce ya samu kiran waya daga mutane daban-daban dangane da labarin ƙarya.

Ya ce ya yi wa Najeriya hidima da tsoron Allah, kuma a shirye ya ke da ya bayar da cikakken bayani akan yadda ya gudanar da NNPC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar jin daɗin alhazai ta Kano ta sanar da kuɗin aikin hajjin badi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta amince...

Kudade: Ganduje ya caccaki Gwamnatin kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Tsohon shugaban jam’iyyar APC...

Gwamnan Kano ya tura sunayen mutane biyu majalisar dokokin don nada su a mukaman Kwamishinoni

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya mika...

NLC Reshen Kebbi Ta Soki Cire Naira Miliyan 14 Daga Albashin Malamai

Kungiyar Kwadago ta Ƙasa (NLC) reshen Jihar Kebbi, ta...