Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

Date:

 

 

Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani tarin taɓo da aka ce an ga sawun Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama a wajen a jihar Kano.

Jaridar Leadership ta rawaito cewa wajen, a unguwar dakata, an share ne domin aikin layin dogo da zai bi ta wajen, amma sai mutane su ka maida shi wani waje mai tsarki na ibada saboda an ga idon ruwa ya na tsatsafowa a daidai wajen wani tarin ƙasa.

IMG 20250415 WA0003
Talla

An ga wani faifen bidiyo da ya karade kafofin sadarwa, inda mutane ke ta tururuwa su na kallo, wasu kuma na yi wa mai tsarki da za su samu albarka da kuma tafiyar zunubai da samun waraka daga cututtuka tunda wai sawun Annabi ne a wajen.

Sai dai kuma tuni hukumar ta Hisbah, ta bakin Mataimakin Kwamandan hukumar, Malam Mujahideen Aminuddeen ya ce an rushe wajen kuma an kori mutane.

InShot 20250309 102403344

A cewar sa, shirme ne da kuma jahilci, duba da cewa Annabi Sallallahu alaihi Wasallama bai taba taka nahiyar Afrika ba.

Malam Mujahideen ya ce irin wannan ta’adar kan janyo Musulmi ya rasa imanin sa, inda ya yi kira ga masu aikata hakan su yi gaggawar tuba su kuma daina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...