Yadda Tinubu ya taimakawa ‘yata ta sami aiki a hukumar kula da harkokin Man Fetur – Buba Galadima

Date:

Buba Galadima, jigo a jam’iyyar NNPP kuma Jagora a cikin tafiyar Kwankwasiyya, ya bayyana yadda ‘yarsa ta samu aiki a Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Najeriya (NUPRC) ta hannun Shugaba Bola Tinubu.

Ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a gidan talabijin na AIT.

InShot 20250309 102403344

Galadima ya ce duk da sukar gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki akai-akai da ya ke yi, har yanzu shi aboki ne ga Shugaba Tinubu.

Tinubu ne ya Gyara min Gidana na Kaduna – Buhari

Ya ce: “Abokai ne mu kuma za mu ci gaba da kasancewa abokai. Idan ina da bukata daga gare shi, zan iya tambaya. Bari in bayyana a gaban al’umma. ‘Yata ta yi amfani da wayata ta kira Shugaban kasa, kuma ya dauka yana tunanin ni ne. Sai suka ce sun kira shi ne saboda rayuwa ta yi tsauri a kasar nan.

FB IMG 1744283415267
Talla

“Suka ce masa ‘Mahaifinmu ba zai iya yi mana wannan ba, amma ya fada mana kai abokinsa ne.’

“Karama daga cikinsu ta ce ta kammala hidimar kasa (NYSC), amma ta kasa samun aiki a Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta ta Najeriya (NUPRC) karkashin jagorancin Gbenga Komolafe. Tinubu kawai, ya kira Komolafe, ya ce ‘je ka ba ‘yar abokina aiki’. Shi ya sa take so ta je Makka domin godewa Allah da kuma godiya ga Shugaban kasa.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...