Yadda Tinubu ya taimakawa ‘yata ta sami aiki a hukumar kula da harkokin Man Fetur – Buba Galadima

Date:

Buba Galadima, jigo a jam’iyyar NNPP kuma Jagora a cikin tafiyar Kwankwasiyya, ya bayyana yadda ‘yarsa ta samu aiki a Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Najeriya (NUPRC) ta hannun Shugaba Bola Tinubu.

Ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a gidan talabijin na AIT.

InShot 20250309 102403344

Galadima ya ce duk da sukar gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki akai-akai da ya ke yi, har yanzu shi aboki ne ga Shugaba Tinubu.

Tinubu ne ya Gyara min Gidana na Kaduna – Buhari

Ya ce: “Abokai ne mu kuma za mu ci gaba da kasancewa abokai. Idan ina da bukata daga gare shi, zan iya tambaya. Bari in bayyana a gaban al’umma. ‘Yata ta yi amfani da wayata ta kira Shugaban kasa, kuma ya dauka yana tunanin ni ne. Sai suka ce sun kira shi ne saboda rayuwa ta yi tsauri a kasar nan.

FB IMG 1744283415267
Talla

“Suka ce masa ‘Mahaifinmu ba zai iya yi mana wannan ba, amma ya fada mana kai abokinsa ne.’

“Karama daga cikinsu ta ce ta kammala hidimar kasa (NYSC), amma ta kasa samun aiki a Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta ta Najeriya (NUPRC) karkashin jagorancin Gbenga Komolafe. Tinubu kawai, ya kira Komolafe, ya ce ‘je ka ba ‘yar abokina aiki’. Shi ya sa take so ta je Makka domin godewa Allah da kuma godiya ga Shugaban kasa.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...