Kisan Gilla: Tawagar Gwamnatin Kano ta sauka a jihar Edo

Date:

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusif ya tura wata tawaga ta musamman zuwa jihar Edo, domin binciken gaskiyar abin da ya faru na kisan gillar da akayiwa mafarauta ƴan asalin Kano a jihar.

An kafa kwamitin tawagar ƙarƙashin jagorancin mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo.

InShot 20250309 102403344

Wata sanarwar da mai magana da yawun mataimakin gwamnan Ibrahim Garba Shu’aibu, ya fitar, ya ce kwamitin ya ƙunshi fitattun mutane daga Kano wanda suka haɗar da Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umar, Kwamishinan harkokin addini, shugaban ƙaramar hukumar Bunkure, Kwamishinar mata, kwamishinan ayyuka na musamman da sauran manyan jami’an gwamnatin Kano.

Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

An dai kafa kwamitin ne domin binciken kisan Hausawa mafarauta ƴan asalin jihar Kano su 16 a garin Uromi na jihar Edo, wanda wasu matasa suka aikata mummunan kisan gillar ga Hausawan.

FB IMG 1744283415267
Talla

Mataimakin gwamnan Kano, ya bayyana cewa zasu yi bakin ƙoƙari wajen tabbatar da adalci ga iyalan waɗanda aka kashe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...