Kisan Gilla: Tawagar Gwamnatin Kano ta sauka a jihar Edo

Date:

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusif ya tura wata tawaga ta musamman zuwa jihar Edo, domin binciken gaskiyar abin da ya faru na kisan gillar da akayiwa mafarauta ƴan asalin Kano a jihar.

An kafa kwamitin tawagar ƙarƙashin jagorancin mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo.

InShot 20250309 102403344

Wata sanarwar da mai magana da yawun mataimakin gwamnan Ibrahim Garba Shu’aibu, ya fitar, ya ce kwamitin ya ƙunshi fitattun mutane daga Kano wanda suka haɗar da Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umar, Kwamishinan harkokin addini, shugaban ƙaramar hukumar Bunkure, Kwamishinar mata, kwamishinan ayyuka na musamman da sauran manyan jami’an gwamnatin Kano.

Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

An dai kafa kwamitin ne domin binciken kisan Hausawa mafarauta ƴan asalin jihar Kano su 16 a garin Uromi na jihar Edo, wanda wasu matasa suka aikata mummunan kisan gillar ga Hausawan.

FB IMG 1744283415267
Talla

Mataimakin gwamnan Kano, ya bayyana cewa zasu yi bakin ƙoƙari wajen tabbatar da adalci ga iyalan waɗanda aka kashe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...