Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Matatar man Ɗangote ta sanar da rage farashin litar man fetur da take siyar wa ƴan kasuwa masu gidajen mai zuwa naira 865 daga naira 880.

Idan za a iya tunawa a Wannan makon ne majalisar zartarwa ta kasa karkashin jagorancin Shugaban Kasa Bola Tinubu ta amine da sayar da danyen man ga matatun mai na cikin gida akan farashin naira.

Kadaura24 ta rawaito wata majiya ce daga matatar ta tabbatar wa da gidan talabijin na Channels hakan, inda ta ce an rage farashin ne a yau Alhamis.

InShot 20250309 102403344

Ragin farashin ya zo ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin matatar Ɗangote da ministan kuɗin Najeriya, Wale Edun a ranar Talata.

Dakatar da Umara: kungiyar kare hakkin dan adam ta Alhakku ta rubutawa Masarautar Saudia Wasika

Bayan taron ne gwamnatin Najeriya ta ce yarjejeniyar siyar wa Dangote ɗanyen mai da naira na nan, kuma za’a ci-gaba da amfani da ita duk da a baya kamfanin NNPCL ya sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar.

FB IMG 1744283415267
Talla

Da wannan matakin ne ake sa ran gidajen man fetur da suke da yarjejeniya da matatar Dangote irin su MRS da Ardova da Heyden da sauransu za su rage farashin litar man fetur ɗinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar samarin Tijjaniyya ta yi Allah – wadai da hukuncin Kotun ECOWAS

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Kungiyar Samarin Tijjaniya ta kasa tace...

Majalisar dokokin Kano da Freedom Radio sun fara musayar kalamai

Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi al'ummar jihar Kano...

2027: Shugabannin APC a Kano ta Kudu sun mika bukatarsu ga Sanata Kawu Sumaila

Shuwagabannin jam’iyyar APC da Sakatarorin su na mazabar Kano...

Tinubu ya sake ƙaddamar da aiki titin Abuja zuwa Kaduna

Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gina...