Kano: Hakimin Bichi da Sarki Sanusi II ya nada ya kama aiki

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Sabon Hakimin Bichi da aka nada, Alhaji Munir Sanusi Bayero, ya ya kama aiki a hukumance, inda ya jaddada muba’arsa ga Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Khalifa Muhammadu Sanusi II tare da yin alkawarin yin adalci ga al’ummarsa

A jawabin da ya gabatar ga al’ummar garin Bichi, Wamban Kano ya bayyana tarihin yadda kakaninsa suka yi hakimcin garin Bichi da kuma alakar Bichi masarautar Kano.

Inda ya ce wasu daga cikin sarakunan Kano da suka shude da suka hada da Sarki Abdullahi Bayero da Khalifa Sir Muhammadu Sanusi duk sai da suka zama hakimai a Bichi sannan suka rike Sarautar Kano.

InShot 20250309 102403344
Talla

Alhaji Munir Sanusi Bayero ya bayyana matukar godiyarsa ga Sarki Muhammadu Sanusi II bisa yadda ya amince da shi har ya dora masa wannan nauyin. Ya bayyana godiya ga Sarki bisa irin goyon bayan da yake na shi goyon baya tun daga nada shi a matsayin Dan Maje har ya kai matsayin Wambai.

FB IMG 1742833592790
Wanban Kano Alhaji Munnir Sanusi da Shugaban karamar hukumar Bichi

Ya kuma bukaci ‘ya’yan Masarautar da su ci gaba da ba da hadin kai da goyon bayan shugabancin Sarkin, inda ya jaddada cewa masarautar Dabo ta kowa ce. Ya yi gargadi game da rarrabuwar kawuna da kuma tasirin waje da ka iya kawo cikas ga daidaiton gidan sarauta.

Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

A matsayinsa na Hakimin Bichi, ya yi alkawarin bin sahun magabatansa, musamman kaninsa, Wambai Abubakar, wajen ba da fifiko kan harkokin ilimi, da ayyukan yi, da walwala. Ya sha alwashin tabbatar da manufar Sarki Sanusi II, na bunkasa ilimi da tabbatar da samar da abinci mai gina jiki ga yara a yankin.

Wambai ya kuma mika godiyarsa ga Gwamna Abba Kabir Yusuf, tare da yaba masa bisa rawar da yake takawa wajen dawo da martabar Masarautar da kuma ciyar da ilimi gaba a jihar Kano. Ya yabawa shugabancin gwamnan tare da jaddada goyon bayansa ga ayyukan cigaban gwamnati a Bichi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...