Gwamnan Kano ya bada guraben aikin gwamnati ga ɗaliban da ya kai ƙasar waje karatu

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ɗauki ɗalibai 54 aiki bayan sun kammala karatun digiri na biyu a kan harkar kiwon lafiya a kasar waje.

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya aikowa Kadaura24.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ya ce gwamnan ya sanar da bada guraben aikin ne a liyafar buɗe-baki da ya yi da daliban, wanda su ka dawo daga India bayan sun yi karatun na shekara ɗaya a jami’ar Symbiosis International University a Ranar Juma’a.

Ya ce tuni an kammala duk wasu tsare-tsare ga ɗaliban na su fara aiki a asibitocin gwamnati domin inganta harkar lafiya a jihar.

Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

Ya kuma hore su da su yi amfani da ƙwarewar da su ka samo lokacin da su ke karatun a India a yayin gudanar da aiyukan su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...