Gwamnan Kano ya nada mataimakin mai magana da yawunsa da wasu mukamai

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nada wasu mukamai da karin girma a wani yunkuri na karfafa harkokin mulki da inganta ayyuka a gwamnatinsa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24.

Wadanda aka nada ko kuma aka karawa mukamai daban-daban sune kamar haka.

InShot 20250309 102403344
Talla

1- An nada Architect Hauwa Hassan Tudun a matsayin Manajan Darakta ta Hukumar Tsara Burane ta Kano (KNUPDA)

2- An nada Mustapha Muhammad a matsayin babban sakataren yada labarai na gwamna kuma mataimakin kakakin mai magana da yawun gwamnatin Kano Sunusi Bature D/Tofa

3- An nada Auwal Lawan Aramposu a matsayin mataimakin Manajan Darakta na Hukumar KAROTA.

4- An nada Dr. Tukur Dayyabu Minjibir a matsayin mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin noma.

Baya ga wadannan muhimman mukamai, Gwamna Yusuf ya amince da karin girma ga wasu manyan jami’ai guda biyu.

Gwamnan Kano ya Bayyana Matsayarsa Game da Hawan Sallah Karama a Jihar

1- Zulaihat Yusuf Aji ta samu mukamin mataimakiyar Manajan Darakta ta gidan radiyon jihar Kano.

2- Injiniya Abduljabbar Nanono ya zama mataimakin Manajan Darakta na KHEDCO.

A yayin da yake taya sabbin wadanda ya nada Murna, gwamnan Kano ya ba su tabbacin goyon bayansa, sannan ya bukace su da su yi aiki tukuru a kan ayyukansu domin bayar da ta su gudummawar don ci gaban jihar Kano

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Salanta A Yau ta raba kayan Sallah ga marayu sama da 200

A wani yunkuri na taimako da jin-kai ga marayu...

Hukumar Shari’ah ta jihar Kano ta rabauta da Bohal na sama da miliyan 10 daga kungiyar Wamy

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Hukumar Shari'ah ta rabauta da Katafaren...

Sanarwa ta Musamman Daga Gwamnatin Jihar Kano

SANARWA !!! kasancewar ranar Asabar, 29 ga watan Maris, 2025,...

Gwamnatin tarayya ta aiyana ranakun hutun Sallah

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranakun Litinin 31 ga watan...