Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

Date:

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare da kafa wuraren bincike domin magance matsalar rashin tsaro da ta biyo bayan kisan wata amarya mai shekaru 22, mai suna Zainab Ibrahim.

An yanke wannan shawara ne a taron da aka gudanar a Hadejia, wanda ya haɗa jami’an majalisar masarautar da hukumomin ƙananan hukumomin Malam Madori da Kirikasamma.

Manufar taron ita ce samo mafita ga matsalolin tsaro da ke ƙara ta’azzara a yankin.

InShot 20250309 102403344
Talla

Da yake jawabi a madadin majalisar masarauta, Galadiman Hadejia, Usman Abdul’aziz, ya nuna damuwa matuƙa game da yawaitar hare-haren da ake kai wa jama’a.

Ya buƙaci shugabannin yankin da su haɗa kai da jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya.

An tsinci gawar Zainab Ibrahim, wacce aka ɗaura mata aure a baya-bayan nan, kwance cikin jini a gidanta da ke unguwar Warware.

Gwamnan Kano ya bayyana abun da gwamnatin za ta yi a filin Idi

Lamarin ya tayar da hankalin al’umma, lamarin da ya tilasta hukumomi ɗaukar matakan tsaro cikin gaggawa.

Bayan tattaunawa, an amince da sanya dokar hana fita daga ƙarfe 12 na dare zuwa 4 na Asuba, tare da kafa wuraren binciken tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugaban Karamar hukumar Wudil ya tallafawa wasu amare da kayan daki

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Shugaban Karamar hukumar Wudil Abba Muhammad...

A Gaggauce: Gwamnan Kano ya dakatar da hadiminsa

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusif ya dakatar da...

Da Ɗumi-Ɗumi: Labarin da ake yadawa kan matsayar siyasa ta ba gaskiya ba ne – Kwankwaso

Tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya yi...

Da dumi-dumi: Gwamnatin Kano ta Haramta “Kauyawa Day”

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Hukumar tace fina-finai da dab'i ta...