Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da aikin tituna 17 a cikin ƙwaryar birnin Kano.

Ya kaddamar da fara aiyukan ne a yau Asabar a shataletalen Club Road a birnin Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce aikin wani ɓangare ne na ƙudurin gwamnatin sa na gyaran birnin Kano, inda ya tabbatar da cewa aikin zai bunƙasa harkokin sufuri da kasuwanci da kuma fito da kimar Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24.

Dan uwan gwamnan Kano ya bar NNPP Kwankwasiyya

Sanarwar ta ce gwamnan ya yi alkawarin za a gudanar da aiki mai inganci wanda al’ummar jihar Kano za su dade suna amfana.

Ya bukaci yan kwangilar da su tabbatar sun yi aiki mai inganci, inda ya ce musu zai rika yi musu ziyarar bazata domin ganin irin aikin da suke gudana, inda ya ba da tabbacin ba zai lamunci aiki da ha’inci ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...