Cin zarafi: Akpabio ya musanta zargin da Sanata Natasha ta yi masa

Date:

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya Godswill Akpabio ya musanta zargin cin zarafi ta hanyar lalata da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi a kansa.

Ya musanta zargin ne a ranar Laraba bayan majalisar ta koma aiki daga gajeren hutun da ta tafi.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanata Akpabio ya nuna rashin jin daɗinsa game da abubuwan da ke yawo a shafukan sada zumunta kan zargin da ake masa inda ya yi watsi da shi baki ɗaya.

“Ban taɓa cin zarafin wata mace ba. Na samu tarbiyya daga mahaifiyata, kuma ina girmama mata. An taɓa ba ni lambar yabo ta gwamnan da ya fi kyautata wa mata a Nijeriya,” kamar yadda Sanata Akpabio ya bayyana.

An sake samu tsaiko a shari’ar neman a hana kananan hukumomin Kano kudadensu

Bayan nan ne sai Sanata Natasha ta miƙe tsaye ta gabatar da korafi a kansa a hukumance a gaban majalisar bisa zarge-zargen da take masa.

A yayin da take gabatar da ƙorafin, ta zargi Akpabio da cin zarafi ta hanyar lalata da amfani da ƙarfin iko ba bisa ƙa’ida ba da kuma tauye mata haƙƙinta na gudanar da ayyukan majalisa.

20250228 181700

Bayan ta gabatar da ƙorafin sai shugaban majalisar ya buƙaci kwamitin majalisar kan kula da ɗa’ar ‘yan majalisa da karɓar ƙorafe-ƙorafe ta yi aiki kan zargin.

Wannan na zuwa ne bayan an shafe kwanaki ana ce-ce-ku-ce kan wannan lamarin bayan Sanata Natasha ta yi wannan zargin a wani gidan talabijin a Nijeriya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

2027: Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa game da kasancewarsa a PDP

  Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin...

Cikakken Bayani Kan Yan Bindigar da Yansanda Su Ka Kama a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar...

Gidauniyar Sheikh Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa magidanta 600 kayan abinchi a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gidauniyar Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa...

Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da...