Da dumi-dumi: Tinubu ya nada Sabon Akanta Janar na Nigeria

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada Shamsedeen Babatunde Ogunjimi a matsayin sabon Akanta Janar na tarayyar Nigerian bayan da aka tantance shi.

Nadin nasa, wanda aka amince da shi a yau, zai fara aiki ne daga ranar 7 ga Maris 2025, ranar da wanda yake kan mukamin Oluwatoyin Madehin zai yi ritaya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Boyo Onanuga ya sanyawa hannu.

InShot 20250115 195118875
Talla

An fara bayyana Ogunjimi mai shekaru 57 a matsayin magajin Madehin a watan Disambar da ya gabata.

Ta tabbata: NNPC ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Sanarwar ta ce sai da shugaba Tinubu ya sa aka bi matakai domin tantance Ogunjimi mai shekaru 57 domin tabbatar da kwarewarsa .

Ogunjimi ya kammala karatunsa na digirin farko a Jami’ar Najeriya, Nsukka, a shekarar 1990, inda ya karanci harkar akanta, sannan kuma ya sami digiri na biyu a fannin Accounting and Finance a Jami’ar Legas.

20250228 181700

Mamba ne a Cibiyar Akantoci ta Najeriya

Shugaba Tinubu ya taya Ogunjimi murna bisa nadin da aka yi masa, ya kuma bukace shi da ya dage domin sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na yi wa Nijeriya hidima cikin gaskiya, kwarewa, da sadaukarwa ga hidimar Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...