Da dumi-dumi: Tinubu ya nada Sabon Akanta Janar na Nigeria

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada Shamsedeen Babatunde Ogunjimi a matsayin sabon Akanta Janar na tarayyar Nigerian bayan da aka tantance shi.

Nadin nasa, wanda aka amince da shi a yau, zai fara aiki ne daga ranar 7 ga Maris 2025, ranar da wanda yake kan mukamin Oluwatoyin Madehin zai yi ritaya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Boyo Onanuga ya sanyawa hannu.

InShot 20250115 195118875
Talla

An fara bayyana Ogunjimi mai shekaru 57 a matsayin magajin Madehin a watan Disambar da ya gabata.

Ta tabbata: NNPC ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Sanarwar ta ce sai da shugaba Tinubu ya sa aka bi matakai domin tantance Ogunjimi mai shekaru 57 domin tabbatar da kwarewarsa .

Ogunjimi ya kammala karatunsa na digirin farko a Jami’ar Najeriya, Nsukka, a shekarar 1990, inda ya karanci harkar akanta, sannan kuma ya sami digiri na biyu a fannin Accounting and Finance a Jami’ar Legas.

20250228 181700

Mamba ne a Cibiyar Akantoci ta Najeriya

Shugaba Tinubu ya taya Ogunjimi murna bisa nadin da aka yi masa, ya kuma bukace shi da ya dage domin sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na yi wa Nijeriya hidima cikin gaskiya, kwarewa, da sadaukarwa ga hidimar Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...