Daga Zakaria Adam Jigirya
Dan majalisar wakilai mai kananan hukumomin Kiru da Bebeji Abdulmumin Jibrin Kofa ya tallafawa al’ummar Mazabar da kudade da sauran kayiyyaki domin saukaka musu a wannan wata na Ramadana.
Akalla mutane maza da mata akalla dubu 10 ne suka amfana da tallafin daga kananan hukumomin Kiru da Bebeji.

Wasu daga mutanen sun amfana da tallafin ₦200,000, wasu kuma ₦100,000, yayin da wasu suka samu₦50,000, wasu kuma ₦20,000, sai wasu kuma₦10,000.
Kotu a Kano ta yankewa wasu ƴan TikTok ɗaurin shekara guda a gidan yari
Haka kuma wasu matasa dubu 2 sun amfana da kayan sana’o’i domin su dogara da kawunansu .
Da yake jawabin a yayin taron dan majalisar ya ce ya ba da tallafin ne domin saukakawa al’ummar yankin na sa.
Ya ce dama duk shekara yana gudanar da irin wannan rabo domin saukaka al’ummar yankin kananan hukumomin Kiru da Bebeji.
Kofa ya ba da tabbacin zai cigaba da tallafawa al’ummarsa, ko da ba lokacin Azumin watan Ramadana ba .