Abdulmumin Kofa ya ba da tallafin Azumi ga mutane 10,000 a Kiru da Bebeji

Date:

Daga Zakaria Adam Jigirya

 

Dan majalisar wakilai mai kananan hukumomin Kiru da Bebeji Abdulmumin Jibrin Kofa ya tallafawa al’ummar Mazabar da kudade da sauran kayiyyaki domin saukaka musu a wannan wata na Ramadana.

Akalla mutane maza da mata akalla dubu 10 ne suka amfana da tallafin daga kananan hukumomin Kiru da Bebeji.

InShot 20250115 195118875
Talla

Wasu daga mutanen sun amfana da tallafin ₦200,000, wasu kuma ₦100,000, yayin da wasu suka samu₦50,000, wasu kuma ₦20,000, sai wasu kuma₦10,000.

Kotu a Kano ta yankewa wasu ƴan TikTok ɗaurin shekara guda a gidan yari

Haka kuma wasu matasa dubu 2 sun amfana da kayan sana’o’i domin su dogara da kawunansu .

20250228 181700

Da yake jawabin a yayin taron dan majalisar ya ce ya ba da tallafin ne domin saukakawa al’ummar yankin na sa.

Ya ce dama duk shekara yana gudanar da irin wannan rabo domin saukaka al’ummar yankin kananan hukumomin Kiru da Bebeji.

Kofa ya ba da tabbacin zai cigaba da tallafawa al’ummarsa, ko da ba lokacin Azumin watan Ramadana ba .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...