Da dumi-dumi: An kama wani shugaban karamar hukuma a Kano

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta kama shugaban karamar hukumar Kiru Abdullahi Mohammed bisa zarginsa da sayar da wani fili da aka tanada don yin filin kwallo a garin Kafin Maiyaki.

A binciken da hukumar ta gudanar, wani kamfani mai suna Mahasum ne ya sayi filayen da aka tanada don yin filin wasan akan kudi sama da Naira miliyan 100, inda aka saka kudaden kai tsaye a asusun shugaban karamar hukumar.

InShot 20250115 195118875
Talla

Da yake tabbatar da kamun, jami’in hulda da jama’a na hukumar, Kabir Abba Kabir, ya bayyana cewa daga 1 ga watan Nuwanba, 2024 wato lokacin da aka rantsar da shi a matsayin shugaban karamar hukumar zuwa ranar 27 ga watan Fabarairu 2025 a Asusun sa kuma tuni hukumar ta kwace kudaden.

Rahotanni sun ce Abdullahi Muhammad na bayar da hadin kai ga masu bincike a kokarin hukumar na bankado bayanan da aka yi na sayar da filin tare da hukunta wadanda suka aikata laifin.

Sabbin Matakan tsaro da ya kamata al’ummar Kano su bi a watan Ramadana -Inji Rundunar Yansanda

Hukumar ta sake jaddada aniyar ta na yaki da cin hanci da rashawa da kuma tabbatar da gaskiya a harkokin mulki, inda a halin yanzu wanda ake zargin yana hannun jami’an tsaro yayin da ake ci gaba da bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...