Yanzu-yanzu: Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Ramadan

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’adu Abubakar III ya bukaci al’ummar Musulmi dake fadin Nigeria da su fita fara duban jinjirin watan Ramadana a gobe JUMA’A 29 ga Watan SHA’ABAN, 1446AH daidai da 28/2/22025.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci na fadar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta ce gobe Juma’a ita ce 29 ga watan sha’aban kuma ita rana ta farko da ya kamata al’ummar Musulmi su fara duba jinjirin watan Ramadana na Wannan Shekarar.

Fargaba: An tsaurara tsaro a Gidan Sarki na Nasarawa inda Aminu Ado Bayero ke zaune

Sanarwar ta ce Idan Allah yasa anga watan sai a sanar da wani basarake mafi kusa domin isar da sakon ga Sarkin Musulmi ko a kira wadannan numbobin domin isar da sakon kai tsaye ga majalisar Sarkin Musulmi.

1.08037157100
2. 08066303077
3. 08035965322
4. 08099945903
5. 07067146900

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...