Yanzu-yanzu: Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Ramadan

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’adu Abubakar III ya bukaci al’ummar Musulmi dake fadin Nigeria da su fita fara duban jinjirin watan Ramadana a gobe JUMA’A 29 ga Watan SHA’ABAN, 1446AH daidai da 28/2/22025.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci na fadar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta ce gobe Juma’a ita ce 29 ga watan sha’aban kuma ita rana ta farko da ya kamata al’ummar Musulmi su fara duba jinjirin watan Ramadana na Wannan Shekarar.

Fargaba: An tsaurara tsaro a Gidan Sarki na Nasarawa inda Aminu Ado Bayero ke zaune

Sanarwar ta ce Idan Allah yasa anga watan sai a sanar da wani basarake mafi kusa domin isar da sakon ga Sarkin Musulmi ko a kira wadannan numbobin domin isar da sakon kai tsaye ga majalisar Sarkin Musulmi.

1.08037157100
2. 08066303077
3. 08035965322
4. 08099945903
5. 07067146900

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...