Majalisar Limaman Masallatan Juma’a ta bayyana goyon bayanta ga matakin gwamnatin na tantance Kungiyoyin farar hula

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Majalisar limaman masallatan Juma’a ta kasa karkashin jagorancin shugabanta Sheikh Muhammad Nasiru Adam, ta bayyana goyon bayanta ga shirin gwamnatin jihar Kano na tantance kungiyoyi masu zaman kansu.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Litinin.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam shi ne babban limamin masallacin Sheikh Ahmad Tijjani dake kofar mata a tsakiyar birnin Kano.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya ce “Muna goyon bayan gwamnatin jihar Kano a kan matakin da ta dauka na tantance kungiyoyi masu zaman kansu.”

InShot 20250115 195118875
Talla

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya jaddada mahimmancin tantance kungiyoyi masu zaman kansu, inda ya bayyana cewa wasu ayyukan kungiyoyin sun sabawa al’ada, da addinin mutanen Kano.

Zargin batanci: Kotu ta aikewa Abdullahi Abbas da Faizu Alfindiki sammaci

Ya bayyana cewa wadannan ayyuka a wasu lokuta suna yin illa ga zamantakewar al’ummar Kano.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya kara da cewa Majalisar Limaman Juma’a ta himmatu wajen aiwatar da ayyukan da suke taimakawa da kuma amfanar addinin Musulunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...

Neman Ilimin addini dana boko da sana’a ba kishiyoyin juna ba ne – Dr. Aminu Sagagi ga matasan Zango

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malamin addinin musulunci a kano...