Gwamnatin Kano ta horar da jami’an yada labaran jihar dabarun sadarwar na zamani

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Kwamishinan Labarai da Harkokin Cikin gida na Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya jaddada ƙoƙarin gwamnatin jihar na bunƙasa ƙwarewa a harkar yaɗa labarai.

Waiya ya bayyana hakan ne a lokacin buɗe taron ƙara wa juna sani na kwana uku game da dabarun aiki ga jami’an labarai daga ma’aikatu da ɓangarori da hukumomi da kuma daga ƙananan hukumomi.

Ma’aikatar ta shirya taron ne da haɗin-gwiwar Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Ƙasa (NIPR) reshen jihar.

InShot 20250115 195118875
Talla

A wata sanarwa da Daraktan Ayyuka na Musamman na Ma’aikatar, Sani Abba Yola ya fitar, ya ce Waiya ya jinjina wa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar bisa amincewa da ɗaukar nauyin shirin, ya na mai bayyana hakan a matsayin nau’in inganta al’umma, wanda kuma ɗaya ne daga cikin jinshiƙan gwamnati ta gari.

Ina farin ciki da saukowar farashin kayan abinchi a Nigeria – Tinubu

A lokacin da ya ke magana a taron, wanda aka yi wa laƙabi da ‘Innovative Approaches Towards Enhancing Pubic Communication in a Digital Age’, ya ce akwai buƙatar jami’an labarai su samu ƙwarewa ta fuskar aiki a zamanance ganin yadda harkar dijital ke bunƙasa.

Ya yi nuni da muhimmancin Soshiyal Mediya da samar da sadarwa mai nagarta ta hanyar tabbatar da dai-dai da isar da labari cikin lokacin da ya dace.

Yanzu-yanzu: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Ya kuma ce, a matsayinsu na waɗanda suke ayyuka tsakanin gwamnati da al’umma yana da kyau a riƙa samun wayar da kan al’umma gami da tabbatar da adalci a yayin ayyukansu.

Kwamishina Waiya ya kuma bayyana farin cikinsa ganin yadda NIPR ta haɗa hannu da gwamnatin wajen inganta aikin yaɗa labarai, ya na mai jaddada aniyarsu ta cigaba da haɗa kai da gidajen jaridu da ƙwararru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...