Ƙungiyar ma’aikatan hukumar kula da kananan hukumomi ta Ƙasa, ta yaba wa gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa nada Alhaji Ibrahim Jibril Fagge, a matsayin Shugaban Hukumar Kula da aiyukan kananan hukumoni ta jihar Kano.
Wannan na kunshe cikin sakon taya murna, da Shugaban Kungiyyar na Kasa Barrister Muhammad Sani Bawa, ya aike wa Alhaji Ibrahim Jibril Fagge.
A sakon, ya jinjinawa gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa farfado da hukumar a jihar Kano, da kuma danka shugabancin hukumar ga Alhaji Ibrahim Jibril Fagge, wanda gogagge ne a aikin-gwamnati, kuma akwai kyakkyawan zaton zai yi abin da ya dace, don ciyar da jihar Kano gaba.

Sanarwar ta kara da cewa, wannan mataki da gwamnan ya dauka, na nuni da irin kokarin gwamnan na bujuro da kyawawan tsare-tsare da za su ciyar da jihar Kano gaba.
Batan Bindigu: Babban Sufeton Yansandan Nigeria ya Roki Majalisa
Shugaban kungiyar Barr. Muhammad Bawa ya yi fatan Alhaji Ibrahim Jibril Fagge zai yi aiki tukuru domin ciyar da jihar Kano gaba, sannan kuma ya fitar da kungiyar kunya.
Kungiyar ma’aikatan hukumar kula da kananan hukumomin ta Kasa dai tana da rassa a dukkanin Jihohi 36 da babban birnin tarayya Abuja.