Batan Bindigu: Babban Sufeton Yansandan Nigeria ya Roki Majalisa

Date:

Sifeto Janar na ƴansanda Najeriya, Kayode Egbetokun ya rubuta wa majalisar dattawa wasiƙa yana roƙonta cewa binciken da za a ci gaba da yi dangane da ɓatan bindigogi 3,907 ya kasance a sirrance bisa dalilan tsaro.

Sai a wasiƙar, sifeto janar na ƴansandan ya yi watsi da rahoton 2019 da ofishin babban mai bincike da gwamnatin tarayya ya fitar wanda ya yi ikrarin ba a san inda dubban bindigogin ƴansanda suka shiga ba ya zuwa watan Janairun 2020 inda ya bayyana rahoton da cewa cike yake da kurakurai.

InShot 20250115 195118875
Talla

Wasiƙar wadda aka karanta ta a majalisar dattawa bayan amince wa da kasafin kuɗin ƙasar na 2025 a ranar Alhamis, na zuwa ne sa’a 48 bayan wani zaman saurare da kwamitin majalisar dattawa mai binciken kashe-kashen kuɗaɗen gwamnati inda rundunar ƴansandan ta yi ta nuƙu-nuƙu wajen kare kanta.

Ba wani maniyaci dan Nigeria da zai rasa Aikin Hajjin bana – Shugaban NAHCON

Sifeto Janar na ƴansandan, kayode Egbetokun wanda ya kasance a wurin sauraron bahasin ranar Talata kafin daga bisani ya nemi uzuri ya bar zaman, ya soki yadda ake neman titsiye rundunar ƴansandan ƙasar a bainar jama’a.

Ya ƙara da cewa bai dace a rinƙa tattuna irin waɗannan batutuwan a bainar jama’a ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...