An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Date:

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya ce ya dakatar da shugaban kungiyar Ahmad Gogel da sakataren kungiyar M I Tudun Wada bisa zarginsu da rashin iya jagoranci da zubar da kimar ofisoshinsu.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka aikowa Kadaura24, mai dauke da sa hannun Najib Bala Salihu (Dawaki),Kabir Waya da Mukhtar Kabir Maitama da Farouk DanBatta.

“Muna amfani da wannan dama domin sanar da ya’yan Wannan kungiya da jagororin Jam’iyyar APC da ma dukkanin al’umma cewa mun dakatar da shugaba da sakatare na wannan kungiyar don haka kar kowa yayi mu’amala da su a matsayin Shugabannin kungiyar APC X Eagle Forum”.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta ce ba a dauki wannan matakin ba sai da aka gudanar da bincike tare da tuntuba wadanda suka dace sannan aka yankin wannan matakin na dakatar da su.

“Za mu nada wadanda za su yi ke matsayin shugaba da sakatare na kungiyar nan gaba kadan, domin cigaba da aiwatar da aiyukan kungiyar da kuma kare martaba da kimar jam’iyyar ta APC da kuma jagororinmu”. A cewar sanarwar

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Sanarwar ta kara da cewa” Mun gamsu da salon jagorancin shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje, sannan muna amfani da wannan dama wajen kara jaddada mubaya’armu ga mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, kuma muna yi masa fatan cikin da yin mulkinsa cikin koshin lafiya”.

“Muna kara jaddada goyon bayanmu ga Jam’iyyar APC da Jagoranta kuma za mu cigaba da yi musu biyayya a kokarinsu na ciyar da jam’iyyar gaba da kuma hada kan ya’yan jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...