Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

 

Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj Ibrahim Imam ya ce za su duba yiyuwar Kara Alwawus din da su ke baiwa Limamai da Ladanai na Karamar hukumar Dala.

Alhaji Suraj Imam ya bayyana hakan ne yayin wani taro da limaman masallatai dake yankin karamar hukumar Dala .

yana Mai cewar tabbas limaman da Ladanai suna da matukar mahinmanci a tsakakanin al’umma.

InShot 20250115 195118875
Talla

Cikin wata sanarwa da Jami’ar Yada labaran karamar hukumar Dala Hassana Aminu ta aikowa Kadaura24, ta ce
Surajo Imam yace ya zama wajibi su sake yin duba akan alawus din da ke basu duk wata su da ladanai da na’ibansu, inda yace za a yi duba da yanayin da ake ciki rayuwa .

Haka Kuma Shugaban karamar hukumar ya karbi kukansu na gabatar da bita akan yadda zasu fahimci abin da ake nufi da gwaji kafin aure idan an gabatar musu da sakamakon .tare da yin kira a gare su akan yiwa shugabanni addu’ar Allah ya taimake su wajen cigaba da gudanar da managartar ayyukun raya kasa .

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Da yake nasa jawabin shugaban limaman masallatai na yankin dala malam Nura Arzai kuma limamin masallacin Ah’hababu na mariya sunusi Dantata dake Kofar Ruwa ya bayyana jin dadinsa bisa wannan gayyatar , inda yace dama jira suke a kira su , sannan zasu cigaba da kokari akan tarbiyantar da yara masu tasowa .

Malam Nura Arzai yace karamar hukumar Dala tana da masallatai guda 34 da limamai da ladanai da na’ibai wanda aka yi su na’ibai na daya da na biyu .

Malam nura arzai yayi kira ga gwamnati data mai da hankali akan gina makarantun kur’ani da islamiyya, inda yace Idan akai hakan tattalin arzikin kasar zai gyaru.

A jawabansu daban-daban imam Bukar Abubakar da imam Isah Abba umar Madabo sun yi kira ga shugaban karamar hukumar Dalan da yaji tsoron Allah yayi mulki bisa gaskiya da amana ya tsaya akan tafarkin da yayi alkhawari .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...