Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano, Alhaji Musa Iliyasu Kwankwaso, ya bukaci gwamnatin jihar Kano da ta biya diyya ga wadanda aka kashe ya’yansu a yayin rushe wasu gine-gine a Rimin Zakara da ke jihar.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar Lahadin da ta gabata ne tawagar jami’an tsaro ta hadin gwiwa suka bude wuta, inda suka kashe mutane hudu tare da raunata wasu da dama a yayin rushe wasu gine-ginen da aka gina ba bisa ka’ida ba a wasu filaye na jami’ar Bayero ta Kano (BUK) .

InShot 20250115 195118875
Talla

Gwamnatin jihar ta bakin kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim Wayya, ya mayar da martani game da kashe-kashen, inda ya ce za a kafa kwamitin da zai binciki lamarin.

Kwankwaso ya ce: “ Ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf da kansa tare da kwamishinonin sa na kasa da ayyuka su kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan mutanen da suka rasa rayukansu a rikicin.

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

“Har ila yau, ya kamata gwamnati ta gaggauta fara biyan diyyar gidaje da gine-ginen da aka rushe tare da biyan diyyar rayukan da aka rasa.

“Na yarda da abun da Amnesty International ta ce na kiran da ta yiwa gwamnatin jihar Kano ta dakatar da kai hare-hare kan al’ummomin da ke fama da talauci wadanda ake azabtarwa shekara da shekaru”. Inji Kwankwaso

Musa Iliyasu Kwankwaso ya ce yana amfani da damar wajen kara mika sakonsa na ta’aziyya ga wandanda aka kashewa ya’yansu da kuma jajantawa mutanen da aka raunata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...