Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano, Alhaji Musa Iliyasu Kwankwaso, ya bukaci gwamnatin jihar Kano da ta biya diyya ga wadanda aka kashe ya’yansu a yayin rushe wasu gine-gine a Rimin Zakara da ke jihar.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar Lahadin da ta gabata ne tawagar jami’an tsaro ta hadin gwiwa suka bude wuta, inda suka kashe mutane hudu tare da raunata wasu da dama a yayin rushe wasu gine-ginen da aka gina ba bisa ka’ida ba a wasu filaye na jami’ar Bayero ta Kano (BUK) .

InShot 20250115 195118875
Talla

Gwamnatin jihar ta bakin kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim Wayya, ya mayar da martani game da kashe-kashen, inda ya ce za a kafa kwamitin da zai binciki lamarin.

Kwankwaso ya ce: “ Ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf da kansa tare da kwamishinonin sa na kasa da ayyuka su kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan mutanen da suka rasa rayukansu a rikicin.

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

“Har ila yau, ya kamata gwamnati ta gaggauta fara biyan diyyar gidaje da gine-ginen da aka rushe tare da biyan diyyar rayukan da aka rasa.

“Na yarda da abun da Amnesty International ta ce na kiran da ta yiwa gwamnatin jihar Kano ta dakatar da kai hare-hare kan al’ummomin da ke fama da talauci wadanda ake azabtarwa shekara da shekaru”. Inji Kwankwaso

Musa Iliyasu Kwankwaso ya ce yana amfani da damar wajen kara mika sakonsa na ta’aziyya ga wandanda aka kashewa ya’yansu da kuma jajantawa mutanen da aka raunata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...