Yanzu-yanzu: Dangote ya karya farashin man fetur

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Matatar mai ta Dangote ta karya farashin man fetur daga Naira 950 zuwa Naira 890 kan kowace lita a yammacin wannan Asabar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban sashin yada labarai da hulda da jama’a na kamfanin Anthony Chiejina ya sanyawa hannu, kuma aka rabawa manema labarai.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar da matatar man ta Dangote ta fitar ta ce sabon farashin zai soma aiki ne daga yammacin wannan Asabar.

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Sanarwar ta ce kamfanin ya rage farashin man ne sakamakon yadda aka sami saukin makamashi a kasuwar duniya, da kuma yadda farashin danyan mai ya sauka.

Kamfanin ya bukaci yan kasuwar dake sayan kayansu da su tabbatar sun rage farashin don al’umman Nigeria su amfana da saukin domin inganta rayuwarsu kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yake fata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...