Tallafawa al’umma: Kungiyar cigaban Unguwar Zango ta Karrama Dr. Muhammad Musa Zango

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Makaman Bichi Alhaji Isyaku Umar Tofa ya bukaci al’umma da suyi koyi da Dr. Muhammed Musa Zango wajan tallafawa al’umma da arzikin da Allah ya ba shi .

Alhaji isyaku Tofa ya bayyana hakan ne yayin taron da kungiyar hadinka cigaban unguwar Zango wato Zango community Development association ta Shirya domin karrama Dr. Muhammad Musa Zango .

Ya ce tabbas abubuwan alkhairin da Dr. Muhammad Zango yake yi abun a yaba ne kuma abun aikoyi da shi ne musamman bisa yadda yake tiritiri da al’umma wajan gina musu rayuwa .

InShot 20250115 195118875
Talla

“Babu shakka al’umma suna cikin mawuyacin hali akwai bukatar masu arziki su rika tallafawa masu karamin karfi, don fitar da su ko rage musu radadin halin da suke ciki”. Inji Alhaji Isyaku Umar

Ya kuma yabawa wannan kungiya bisa karramawar da ta yiwa Dr. Muhammad Zango, inda ya ce hakan zai kara masa kwarin gwiwar cigaba da tallafawa al’umma.

Musa Iliyasu ya bayyana dalilin da yasa Kwankwaso ke neman komawa APC yanzu

A nasa jawabin guda cikin wadanda suka shirya taron Hon. Shu’aibu Idiris Zango ya ce sun karrama Dr. Muhammad Musa Zango saboda irin gudunmawar da yake basu da sauran al’umma .

“Mu shirya masa wannan taron karramawar ne musamman saboda yadda shi a karankansa ya kafa Gidauniyar tallafawa al’umma a unguwar Zango wacce ake Kiran da FATAH ZANGO FONDATION Kuma ya asasata shi kadai ba tare da wani ba”.

Shu’aibu Idiris Zango ya godewa mahalarta taron, sannan ya yi kira ga sauran masu hannu da shuni da su rika tallafawa masu karamin karfi don saukaka musu.

APC ta kori tsohon ministan Buhari

Da yake nasa jawabin wanda aka shirya taron domin shi Dr. Muhammed Musa Zango ya nuna farin cikinsa bisa wannan karramawa da aka yi masa, sannan ya ce hakan zai kara masa kwarin gwiwar cigaba da tallafawa al’umma.

” Yanzu nan, Ina sanar da cewa duk masu fama da lalurar idanu su zo su karbi kati domin a duba su kuma a basu magani kyau nan take”. Inji Dr. Muhammad Musa Zango

Daga karshe ya kara dace wa ba zai taba gajiyawa ba wajen taimakan al’umma, inda kuma ya yabawa kungiyar bisa karramawar da ta yi masa, sannan ya basu tabbacin kofarsa a bude take domin cigaba da tallafawa al’umma.

Itama Anata bangaran uwar gidan Dr. Muhammed Musa Zango Barr. Hajiya Mardiyya Bashir salihi Magashi ta ce a shirye take ako da yaushe domin karfafawa mai gidanta gwiwa domin ya cigaba da rubanya aiyukan alkhairin da ya saba yi wa al’umma.

Taron dai ya gudana ne a Sani Abacha Stadium kofar Mata, taron ya samu halartar manyan Baki daban-daban daga ciki da wajan jihar Kano

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya karya farashin man fetur

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Matatar mai ta Dangote ta karya...

APC ta kori tsohon ministan Buhari

Jam'iyyar APC ta kori tsohon gwamnan jihar Osun kuma...

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Mai baiwa gwamnan Kano shawara na...

Musa Iliyasu ya bayyana dalilin da yasa Kwankwaso ke neman komawa APC yanzu

Babban Daraktan kudi na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama'are kuma...