Musa Iliyasu ya bayyana dalilin da yasa Kwankwaso ke neman komawa APC yanzu

Date:

Babban Daraktan kudi na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are kuma jigo a jam’iyyar APC, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya yi zargin cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran dariƙar Kwankwasiyya na yunkurin daidaitawa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya samu nasarar yin wa’adi na biyu na mulkin jihar a 2027.

InShot 20250115 195118875
Talla

Daily Trust ta rawaito cewa da ya ke zantawa da manema labarai a Kano a ranar Alhamis, Iliyasu, tsohon kwamishina ne a Kano , ya yi ikirarin cewa Kwankwaso na yunkurin komawa jam’iyyar APC ne domin buƙatar sa ta siyasa.

Ya kuma gargadi Tinubu da kada ya amince da Kwankwaso, domin “zai ci amanar sa a siyasa” kamar yadda ya yi wa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a baya.

Musa Iliyasu Kwankwaso dai ya jima yana adawar siyasa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...