Musa Iliyasu ya bayyana dalilin da yasa Kwankwaso ke neman komawa APC yanzu

Date:

Babban Daraktan kudi na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are kuma jigo a jam’iyyar APC, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya yi zargin cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran dariƙar Kwankwasiyya na yunkurin daidaitawa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya samu nasarar yin wa’adi na biyu na mulkin jihar a 2027.

InShot 20250115 195118875
Talla

Daily Trust ta rawaito cewa da ya ke zantawa da manema labarai a Kano a ranar Alhamis, Iliyasu, tsohon kwamishina ne a Kano , ya yi ikirarin cewa Kwankwaso na yunkurin komawa jam’iyyar APC ne domin buƙatar sa ta siyasa.

Ya kuma gargadi Tinubu da kada ya amince da Kwankwaso, domin “zai ci amanar sa a siyasa” kamar yadda ya yi wa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a baya.

Musa Iliyasu Kwankwaso dai ya jima yana adawar siyasa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...