Musa Iliyasu ya bayyana dalilin da yasa Kwankwaso ke neman komawa APC yanzu

Date:

Babban Daraktan kudi na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are kuma jigo a jam’iyyar APC, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya yi zargin cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran dariƙar Kwankwasiyya na yunkurin daidaitawa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya samu nasarar yin wa’adi na biyu na mulkin jihar a 2027.

InShot 20250115 195118875
Talla

Daily Trust ta rawaito cewa da ya ke zantawa da manema labarai a Kano a ranar Alhamis, Iliyasu, tsohon kwamishina ne a Kano , ya yi ikirarin cewa Kwankwaso na yunkurin komawa jam’iyyar APC ne domin buƙatar sa ta siyasa.

Ya kuma gargadi Tinubu da kada ya amince da Kwankwaso, domin “zai ci amanar sa a siyasa” kamar yadda ya yi wa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a baya.

Musa Iliyasu Kwankwaso dai ya jima yana adawar siyasa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...