Kaso 30% ne kacal na mata ke haihuwa a asibiti – Gwamnatin Kano

Date:

Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, ya bayyana damuwarsa game da yadda ya ce kashi 30 ne kacal na mata a Jihar Kano ne ke haihuwa a asibiti, wani al’amari da ke bada gudunmawa wajen yawaitar mace-macen mata masu juna biyu a Jihar.

Ya jaddada cewa yawan mace-macen mata masu juna biyu a Najeriya ba abin abinda za a amince dashi ba ne.

InShot 20250115 195118875
Talla

Dakta Yusuf ya yi wannan bayani ne a jiya Litinin yayin wani taron bita da aka gudanar a Bristol Palace a Kano mai taken “Matakin Rage Mace-Macen Mata Masu Juna Biyu da Jarirai.”

Jaridar Tribune ta rawaito Kwamishinan na bayyana cewa, “Dole ne mu haɗa kai domin tabbatar da cikar burin gwamnatin tarayya na rage mace-macen mata masu juna biyu a kasar nan.

Tafiyar Kwankwasiyya a wajena tamkar ibada ce – Abubakar Adamu Rano

“Jihar Kano tana da muhimmanci sosai idan aka yi la’akari da alamu na bangaren kiwon lafiya da kuma matsalolin da ke addabar wannan bangare.

“Domin Kano, wacce ita ce jiha mafi yawan jama’a a kasar, ana samun yawan mace-macen mata masu juna biyu da jarirai, wanda ya hana ni da gwamna samun barci tun lokacin da muka hau kan mulki,” in ji Yusuf.

A cewar Kwamishinan Lafiya, gwamnatin Jihar Kano a kokarinta ta kirkiro da tsarin bayar da kulawar haihuwa kyauta ga mata masu juna biyu tare da samar da kayan aiki ga sama da cibiyoyin kiwon lafiya 60 da kuma cibiyoyin kula da lafiya na matakin farko guda 63.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...