Gwamnatin Kano Za Ta Fara Shirin Yiwa Ali Madakin Gini Kiranye

Date:

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya ce zai jagoranci yiwa dan majalisarsu na tarayya Hon. Ali Sani Madakin Gini kiranye daga Majalisar , sakamakon al’ummar karamar Hukumar Dala da Kano basa bukatar wakilcinsa.

Kadaura24 ta rawaito Kwamared Waiya ya bayyana haka ne yayin taron masu ruwa da tsaki na karamar Hukumar Dala da Yan jamiyyar NNPP, Wanda aka gudanar a dakin taro na Mumbayya dake nan Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce karamar Hukumar Dala tana bukatar jagora jajirtacce Wanda zai Kai matsalolin al’ummar yakin Majalisar wakilai domin a magance su.

Kaso 9.6% na daliban firamare a Kano suka iya karatu – UNICEF

Kwamishinan ya kuma godewa Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa tarin mukaman da ya baiwa wadanda suka fito daga karamar hukumar Dala.

Taron ya samu halartar Shugabannin jam’iyyar NNPP na karamar Hukumar Dala da sauran masu ruwa da tsaki na tafiyar Kwankwasiyya a karamar hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...