Za mu karasa Aikin tashar tireloli ta Dakatsalle, Gundutse da Ganduje ya yi watsi da su – Gwamnan Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana shirin farfado da tashar tireloli da aka yi watsi da su a shiyyar Kano ta Kudu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya aikowa, gwamnan ya bayyana hakan ne biyo bayan ziyarar bazata da ya kai wurin dake Dakatsalle, daya daga cikin wuraren da aka yi watsi da aikin.

Sanarwar ta kara da cewa tun a shekarar 2014 ne aka fara gudanar da aikin tashar tirelolin a gwamnatin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, inda aka tsara tashar a wurare uku dake Dakatsalle, Gundutse, da Dawanau.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sai dai kuma an yi watsi da ayyukan a lokacin gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje.

Gwamna Yusuf ya bayyana damuwarsa kan yadda ababen hawa ke yawan toshe hanyoyi, lamarin da ke kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa da kuma kawo cikas ga masu amfani da hanya a fadin birnin jihar.

Gwamna Kano ya kaddamar da aikin titi mai tsawon kilomita 5 a garin Dawakin Tofa

Gwamnan ya nanata kudirin gwamnatinsa na kammala aikin tashar tirelolin dake Dakatsalle da Gundutse don rage cunkoson ababen hawa, da bunkasa tattalin arziki a jihar.

Gwamnan ya yi Allah wadai da abin da gwamnatin da ta gabata ta yi, inda ya bayyana shi a matsayin barna da rashin kishin kasa.”

Ya soke duk wani fili da gwamnatin data gabata ta bayar a wuraren da za a yi tashar tirelolin.

Ya ba da tabbacin idan an kammala aikin za a mika tashar ga kungiyar masu harkokin sufuri NATO don cigaba da kula da wuraren.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...