Kwamishina Waiya ya karbi bakuncin Shugabannin Jaridar Daily trust

Date:

Daga Aisha Muhammad Adam

 

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya jaddada kudirinsa na aiki kafada da kafada da masu ruwa da tsaki a fannin yada labarai domin cimma manufar da ta sa aka samar da ma’aikatar.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne yayin da ya karbi bakuncin Shugabannin gidan jaridar Daily trust, wadanda suka je domin taya shi murnar mukamin da gwamnan Kano ya ba shi.

InShot 20250115 195118875
Talla

Yayin ziyarar Kwamared Waiya ya bayyana cewa suna da kyakykyawa kuma dadaddiyar alakar aiki tsakanin shi da Daily trust , har sai da tuna musu irin gudunmawar shawarwari da ya bayar domin bude talabijin dinsu na Trust Tv.

Ya yabawa gidan jaridar bisa irin gudunmawar da suke bayarwa wajen yada labarai da kuma kokarin da suke na an Karar da gwamnati irin nauyin al’umma dake kansu.

Tallafin N30m: EFCC da hukumar yaki da rashawa ta Kano sun karbi korafi kan wasu hadiman gwamnatin Kano

Waiya ya gode musu bisa ziyarar sannan ya basu tabbacin yin aiki tare domin yada manufofin gwamnatin jihar Kano dake karkashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf.

A nasa jawabin tun da fari, Babban jami’in kamfanin Media trust Ahmad Ibrahim Shekarau ya yabawa gwamnan Kano bisa duba chanchantar Waiya har ya nada shi a matsayin kwamishinan yada labarai.

Ya ba da tabbacin za a cigaba da kyautata alakar dake tsakaninsu da gwamnatin jihar Kano Wanda ya ce duk sati ma akwai wani shiri da suke yiwa gwamnatin a Tv, wanda ke yada manufofin gwamnatin Kanon.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...