Shin ko kun san ƙi taimakon ɗansanda’ a Nigeria laifi ne?

Date:

Rundunar ƴansandan Najeriya ta tunatar da al’ummar ƙasar cewa mutanen da suka ƙi taimakon jami’anta a lokacin da suke neman ɗauki, na iya fuskantar hukuncin ɗauri ko kuma tara.

A cikin wani bayani da rundunar ta wallafa a shafinta na X, rundunar ta ce wannan na ƙunshe ne a sashe na 99 na dokar ƴansanda ta ƙasar ta shekarar 2000.

Talla

“Duk wanda aka kira domin ya taimaka wa jami’in ɗansanda wanda – a sa’ilin gudanar da aikinsa ke fuskantar cin zarafi ko hantara ko turjiya – sai mutum ya ƙi, ko kuma ya yi watsi da buƙatar taimakawa, to wannan mutum ya aikata laifi, wanda zai iya janyo a yanke masa tarar naira 100,000 ko ɗaurin wata uku, ko kuma duka biyun idan aka same shi da laifi,” kamar yadda bayanin ya nuna.

Iftila’i: Yan ɗaurin aure 19 daga Kano sun kone a hatsarin mota a Filato

Rundunar ƴansandan Najeriya ɗaya ce daga cikin hukumomin tsaro da kundin tsarin mulkin ƙasar ya dora wa nauyin tabbatar da doka a cikin al’umma.

Sai dai sau da yawa an sha kokawa kan yadda jami’anta ke gudanar da ayyukansu.

Wannan ne ma ya haifar da ɗaya daga cikin zanga-zanga mafi muni da aka taɓa yi a ƙasar, inda a cikin shekara ta 2020 matasa suka gudanar da zanga-zangar domin nuna adawa da ‘zaluncin’ wani ɓangare na rundunar, wanda ake yi wa laƙabi da SARS.

Lamarin da ya yi sanadiyyar rushe ɓangaren.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...