Kwamishina a Kano ya mayar da rarar Naira Miliyan 100 Asusun Gwamnati

Date:

 

Sabon Kwamishinan Ƙananan Hukumomi na jihar Kano, Alhaji Tajuddin Usman ya mayar da Naira miliyan 100 ga asusun gwamnatin jihar.

Usman ya mayar da kuɗin ne na rarar kuɗaɗen kwangilar dinka tufafin makaranta ga ɗaliban firamare dubu 789 a fadin ƙananan hukumomi 44 na jihar.

Talla

Kwamishinan, wanda shi ne shugaban kwamitin raba kayan, ya mayar da rarar kudaden da aka ware domin ɗinkawa daliban firamare sabbin tufafin makaranta, inda kuɗaɗen su ka yi ragowa bayan da aka kammala aiki kuma shugaban kwamatin ya kuma dawo dasu.

Rahma Radio ta rawaito cewa Usman ya bayyana hakan yayin kaddamar da rabon kayan a gidan gwamnatin Kano a jiya Litinin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...