Iftila’i: Yan ɗaurin aure 19 daga Kano sun kone a hatsarin mota a Filato

Date:

Mahalarta ɗaurin aure mutum 19 daga Jihar Kano sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota a yankin Kwanar Maciji da ke Ƙaramar Hukumar Pankshin a Jihar Filato.

Mutum 11 daga cikinsu sun tsallaka rijiya da baya da raunuka a haɗarin da ya ritsa da su a yayin da suke hanyar komawa gida bayan ɗaurin auren da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Barikin Ladi a ranar Asabar.

Talla

Shugaban Ƙaramar Hukumar Pankshin, John Dasar, ya bayyana cewa motar matafiyan ta kama da wuta ne, amma an yi nasarar ceto direban da wasu fasinjoji.

Kwamishina a Kano ya mayar da rarar Naira Miliyan 100 Asusun Gwamnati

Ya ce, “an ceto mutane 11 amma mutane 19 sun kone ƙurmus ba za a iya gane su ba, saboda bayan mutane sun zo ana ƙoƙarin ceto fasinjojin ne motar ta kama da wuta, ta cinye ragowar.”

Ya ce an kai waɗanda suka tsira Babban Asibitin Pankshin inda ake duba lafiyarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...