Da dumi-dumi: Bayan tsige Kakakinta Majalisar dokokin Lagos ta zabi sabuwar shugabar majalisar

Date:

Mojisola Meranda ta zama sabuwar shugabar majalisar dokokin jihar Legas bayan tsige Mudashiru Obasa daga mukamin.

Kafin ta zama shugabar majalisar, Meranda ita ce mataimakiyar kakakin majalisar.

Meranta ta zama shugabar majalisar dokokin jihar ne biyo bayan tsige Mudashiru Obasa a matsayin shugaban majalisar saboda zargin rashin da’a da kuma cin zarafi.

Talla

SaharaReporters ta ruwaito a watan Disamba 2024 cewa Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta shigar da kara domin ta binciki Obasa kan zargin karkatar da kudi, da cin amanar jama’a, da kuma cin zarafi.

Rubabbun yan Kwankwasiyya Sanata Barau yake karba – MD Radio

Wata kara da kungiyar Progressive Youth Movement na Ikeja, jihar Legas ta shigar, ta zargi Obasa da yin amfani da wasu kamfanoni wajen wawure kudaden majalisar dokokin Legas da kuma saba ka’idojin saye da sayarwa.

Kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ta bukaci EFCC ta binciki majalisar dokokin Legas kan amfani da Naira biliyan 17 wajen gina kofar gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...