Da Dumi-Dumi: Kotun Daukaka Kara ta Yanke Hukuncin akan shari’ar Masarautar Kano

Date:

Kotun daukaka kara dake zaman ta a Abuja ta yanke hukuncin cewa babbar kotun tarayya ba ta da hurumin saurarar duk wata kara da ta shafi dokar masarautu.

Haka zalika kotun ta ce sashi na 251 na kundin tsarin mulkin Nigeria ya yayi bayani dalla-dalla kan harancin kotun tarayya ta shiga al’amarin da ya masarautu.

Majiyar Kadaura24 ta Justice watch ta rawaito Batun tauye hakkin dan Adam kuwa Kotun daukaka karar ta ce Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya gaza gabatar da hujjojin da za su gasgata da’awarsa.

Talla

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito ce Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero bayan da gwamnatinsa Kano ta ayyana cire shi, ya garzaya gaban babbar kotun tarayya dake Kano domin kalubalantar matakin gwamnatin.

Aminu Ado Bayero yana da’awar cewa an take masa hakkinsa a matsayinsa na dan adam, don haka yake neman kotun da duba labarin, sai dai gwamnatin Kano ta ce kotun tarayyar bata da hurumin saurarar kara lamarin da yasa ta tafi kotun daukaka kara domin nemo fassara.

Rashin biyan yan fasho hakkokinsu tsahon mulkin Ganduje ya jawo wa kano talauci mai yawa – Abba Kabir Yusuf

Kotun daukaka Karar ta ce Babbar kotun tarayyar ba ta da hurumin kamar yadda kotun koli ta Kasa ta taba yanke hukuncin akan shari’ar Tukur da gwamnan gongola.

Kotun ta ce kotun da ke da hurumin shari’ar masarautu a tsarin mulkin Nigeria, ita ce babbar kotun jiha ce ba babbar kotun tarayya ba,

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...