Kotun Daukaka Kara ta Bayar da Umarnin Sake Sauraron Shari’ar Masarautar Kano

Date:

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta bayar da umarnin sake sauraron shari’a kan rikicin masarautar Kano da ya hada da Alhaji Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi.

Kotun daukaka kara, a hukuncin da ta yanke a yau, ta ce ba’a yi wa Aminu Ado Bayero adalci ba saboda yadda wata babbar kotun Kano ta gudanar da shari’a a kansa.

Talla

Mai shari’a Mohammed Mustapha wanda ya yanke hukuncin, ya bayyana cewa babbar kotun Kano ba ta yi wa Aminu Ado Bayero adalci ba ta hanyar gudanar da shari’a ba tare da bashi damar bayanin nasa bangaren ba.

Da Dumi-Dumi: Kotun Daukaka Kara ta Yanke Hukuncin akan shari’ar Masarautar Kano

Mai shari’a Mustapha ya ce ya zama wajibi dukkan kotuna su tabbatar da adalci ga kowane bangare ta hanyar ba su dama daidai gwargwado.

Domin haka kotun daukaka kara ta bayar da umarnin a mika karar ga babban alkalin alkalai na jihar Kano domin baiwa wani alkali damar yanke hukunci na adalci cikin gaggawa.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a watannin baya wata babba kotun jihar kano karkashin jagorancin ta Justice Amina Aliyu ta yanke hukuncin cewa kada Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya sake ayyna kansa a matsayin Sarkin Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...