Rashin biyan yan fasho hakkokinsu tsahon mulkin Ganduje ya jawo wa kano talauci mai yawa – Abba Kabir Yusuf

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya zargi tsohon gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje da kin biyan yan fasho hakkokinsu tsahon shekaru 8 wanda hakan ya jawo talauci jihar.

Ya ce sakacin gwamnatin Ganduje na kin biyan yan fasho da wadanda suka mutu a bakin aiki ne ya jawo suka biyo gwamnatin Kano kudaden da yawansu ya kai biliyan 48.

Talla

Gwamnan Yusuf ya yi wannan zargin ne lokacin da yake jawabi a wajen kaddamar da biyan yan fasho hakkokinsu kashi na uku, a aka sake ware musu Naira Biliyan 5 domin rage basussukan da suke bin gwamnati.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24, yace gwamnan ya tausayawa yan fashon saboda bakar wahalar da suka sha a tsahon shekaru 8 na mulkin Ganduje.

A karon farko bayan cire shi daga sakataren gwamnatin Kano Baffa Bichi ya Magantu

Yace biyan akalla Naira biliyan 16 ga yan fasho kimanin 6,886 na daga kokarinsa na cika alkawuran da ya yi lokacin yakin neman zaben 2023. Inda ya ba da tabbacin zai cigaba da biyan hakkokinsu don inganta rayuwarsu.

Gwamna Yusuf ya kuma yi amfani da bikin wajen sanar da karin kudin fansho na wata-wata daga Naira dubu 5 zuwa Naira dubu 20. Ya ce ya yi hakan ne saboda yadda kayan masarufi ya tashi rayuwa kuma ta yi tsada.

Tun da farko a jawabinsa shugaban kungiyar Malamai ta Kasa Com. Titus Audu Amba, ya yabawa gwamnan bisa biyan hakkokin wadanda suka ga aiki da wadanda suka riga mu gidan Gaskiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...